Hadiza Aliyu an fi saninta da Hadiza Gabon (An haife ta a ranar ɗaya ga watan Yunin shekarar alif ta 1989) a ƙasar Gabon, Hadiza Aliyu ta Kasance Shahararriyar 'yar wasan kwaikwayo ce a masana'antar finafinai ta Kannywood dake Najeriya.
Yau 27 ga watan Yuli na 2022
Ga wasu muhimman abubuwa na tarihi da suka faru a wannan rana.
1996 - A rana irin ta yau a shekara ta 1996 wani bututun mai ya fashe a filin shakatawa na Olympic Centennial da ke birnin Atlanta na kasar Georgia, inda ya kashe mutum 1 tare da raunata mutane 111 a harin ta'addanci na farko da aka yi a gasar Olympics tun bayan gasar 1972 a birnin Munich na Yammacin Jamus.
1953 - An rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da makamai da za ta kawo karshen yakin Koriya a P'anmunjŏm da ke tsakiyar Koriya.
1919 - Rikici ya ɓalle a Chicago bayan da aka sace tare da ɓatar da wani matashi Bakar fata kuma aka nutsar da shi a tafkin Michigan saboda yin iyo a wani yanki da aka kebe don farar fata kaɗai
1214 - A yakin Bouvines, Sarkin Faransa Philip II ya yi nasara a kan kawancen kasa da kasa karkashin jagorancin Sarkin Roma mai tsarki Otto IV.
2012 - Sarauniya Elizabeth ta biyu a hukumance ta bude gasar Olympics ta lokacin bazara ta 2012 a London
Wannan dai shi ne karo na 3 da birnin Landan ke karɓar baƙuncin gasar wasanni ta ƙasa da ƙasa da dama. An kira bikin ne Isles of Wonder kuma Danny Boyle ne ya ba da umarni
1985 - juyin mulki a Uganda Tito Lutwa Okello, wani hafsan sojan Uganda ya yi nasarar yin juyin mulki kan shugaba Milton Obote. Shugaban kasar mai ci Yoweri Museveni ya hambarar da shi bayan watanni 6.
Kwale kwale mafi tsufa da aka taɓa ganowa a nahiyar Afrika, kuma na uku mafi tsufa a duniya shine wanda wani bafulatani ya gano a shekara ta 1987 a ƙyauyan Dunfuna dake ƙaramar hukumar Fume dake jihar Yobe.
A shekara ta 1967, shugaban Najeriya Yakubu Gowon ya raba shiyoyin Najeriya zuwa Jihohi goma sha biyu.
Ƙasar Thailand itace kawai ƙasar da turawa basu yiwa mulkin mallaka ba a yankin kudu maso gabashin Asiya.
Mutanen ƙasar Holand sune suka fi tsawo a duniya.
Ƙasar Brazil itace tafi samar da lemu a duniya.
Tsohon shugaban Najeriya Janaral Murtala Mohammed shine ya kafa tubalin gina babban birnin Tarayyar Najeriya wato Abuja saboda babban birnin Nigeria a wancan lokacin wato Lagos yana fama da cunkoson jama'a. Ya zaɓi tawagar mutane bisa jagorancin mai shari'a Akinola Aguda wanda ya zaɓi Abuja a matsayin sabon gurin da za'a gina babban birnin Nigeria
Kashi ishirin da uku ne kawai na mutanen ƙasar New Zealand suke haihuwar sama da 'ya 'ya biyu.
Rundunar ‘yan sandan Jihar Kwara ta cafke wani matashi bisa zargin laifin yin garkuwa da mahaifinsa har da karɓar kuɗin fansa na Naira miliyan biyu da rabi.
Kotun Ɗaukaka Ƙara ta soke Hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ta haramta wa Jam’iyyar PDP shiga zaɓen Gwamnan Jihar Zamfara a 2023.
Yan sandan kasar Ghana, sun tabbatar da kama wani fitaccen mai fafutuka da ya jagoranci zanga-zangar adawa da gwamnatin Shugaba Nana Akufo-Addo bayan ya yi tsokaci a shafukan sada zumunta game da yunkurin juyin mulki.
Dakarun da ke biyayya ga ƙasar Rasha a Ukraine sun ce sun kakkaɓo wani jirgi maras matuƙi da aka yi niyyar kai musu hari da shi a sansaninsu da ke garin Sevastopol.
Mutum aƙalla biyar ne suka mutu sanna wasu goma suka ɓace bayan jirgin ruwan da ke ɗauke da wasu ƴan ci-rani ya nitse a kusa da ƙasar Tunisiya.
Ɗan takarar kujerar Majalisar Wakilai na jam'iyyar PDP a mazaɓar Birnin Kebbi da Kalgo da Bunza da e Jihar Kebbi, Abba Muhammed Bello, ya rasu.