Shehu Usmanu Ɗan Fodiyo (An haife shi ne a ranar 15, ga watan Disamba a Shekara ta alif 1754 a garin Gobir - Ya rasu a ranar: 20, ga watan Afrilu shekara ta alif 1817 a cikin garin Sokoto)an rada sunan Usman bin Fodiyo , (da Larabci: عثمان بن فودي, Shaikh Usman Ibn Fodiyo, mahaifin Shehu Usman Dan Fodiyo shi ake kira da Malam Muhammad Bello, tare da mahaifiyar sa me suna Maimunatu), Usman Dan fodiyo yana da yara guda biyu mace da namiji. Wanda ya haɗa da Muhammadu Bello da kuma yarsa me suna Nana, Asma'u
Yau 27 ga watan Yuli na 2022
Ga wasu muhimman abubuwa na tarihi da suka faru a wannan rana.
1996 - A rana irin ta yau a shekara ta 1996 wani bututun mai ya fashe a filin shakatawa na Olympic Centennial da ke birnin Atlanta na kasar Georgia, inda ya kashe mutum 1 tare da raunata mutane 111 a harin ta'addanci na farko da aka yi a gasar Olympics tun bayan gasar 1972 a birnin Munich na Yammacin Jamus.
1953 - An rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da makamai da za ta kawo karshen yakin Koriya a P'anmunjŏm da ke tsakiyar Koriya.
1919 - Rikici ya ɓalle a Chicago bayan da aka sace tare da ɓatar da wani matashi Bakar fata kuma aka nutsar da shi a tafkin Michigan saboda yin iyo a wani yanki da aka kebe don farar fata kaɗai
1214 - A yakin Bouvines, Sarkin Faransa Philip II ya yi nasara a kan kawancen kasa da kasa karkashin jagorancin Sarkin Roma mai tsarki Otto IV.
2012 - Sarauniya Elizabeth ta biyu a hukumance ta bude gasar Olympics ta lokacin bazara ta 2012 a London
Wannan dai shi ne karo na 3 da birnin Landan ke karɓar baƙuncin gasar wasanni ta ƙasa da ƙasa da dama. An kira bikin ne Isles of Wonder kuma Danny Boyle ne ya ba da umarni
1985 - juyin mulki a Uganda Tito Lutwa Okello, wani hafsan sojan Uganda ya yi nasarar yin juyin mulki kan shugaba Milton Obote. Shugaban kasar mai ci Yoweri Museveni ya hambarar da shi bayan watanni 6.
Kwale kwale mafi tsufa da aka taɓa ganowa a nahiyar Afrika, kuma na uku mafi tsufa a duniya shine wanda wani bafulatani ya gano a shekara ta 1987 a ƙyauyan Dunfuna dake ƙaramar hukumar Fume dake jihar Yobe.
A shekara ta 1967, shugaban Najeriya Yakubu Gowon ya raba shiyoyin Najeriya zuwa Jihohi goma sha biyu.
Ƙasar Thailand itace kawai ƙasar da turawa basu yiwa mulkin mallaka ba a yankin kudu maso gabashin Asiya.
Mutanen ƙasar Holand sune suka fi tsawo a duniya.
Ƙasar Brazil itace tafi samar da lemu a duniya.
Tsohon shugaban Najeriya Janaral Murtala Mohammed shine ya kafa tubalin gina babban birnin Tarayyar Najeriya wato Abuja saboda babban birnin Nigeria a wancan lokacin wato Lagos yana fama da cunkoson jama'a. Ya zaɓi tawagar mutane bisa jagorancin mai shari'a Akinola Aguda wanda ya zaɓi Abuja a matsayin sabon gurin da za'a gina babban birnin Nigeria
Kashi ishirin da uku ne kawai na mutanen ƙasar New Zealand suke haihuwar sama da 'ya 'ya biyu.
A Jihar Neja dake tsakiyar Najeriya kuma ƴan bindiga sun sako ɗaliban islamiyya da sukayi garkuwa da su bayan watanni uku da kama su. Yaran su 93 dake karatu a Makarantar Salihu Tanko dake garin Tagina an sako su ne ranar 26 ga Watan Agusta.
Bayan Harin da ƴan bindiga suka kai a makarantar horar da Hafsoshin Sojin Najeriya dake Jihar Kaduna An Rufe Kasuwannin Da Ke Kusa yankunan da abin ya faru.
A Jihar Zamfara kuwa Wasu mutanen ƙayukan jihar Zamfara a Arewacin Najeriya sun tara wa ƴan bindiga kuɗi domin neman samun zaman lafiya da tsira da rayukansu.
Wata kotu a Zimbabwe' ta ce za a iya tono gawar tsohon shugaban kasar marigayi Robert Mugabe bayan wani basaraken gargajiya ya ce binnewar da aka yi masa ta keta dokokin al'adunsu. An binne marigayi Mugabe, wanda ya mutu a shekarar 2019 yana da shekara 95 a Maƙabartar su ta ahalin su. Sai dai a watan Mayu wata kotu ta saurari karar da wani basarake ya shigar yana mai cewa binnewar da aka yi masa ta karya dokokin al'adunsu.